✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Cibiyar NITT ta gwada tashin jiragen da ta kera marasa matuka

Cibiyar Koyar da Harkokin Sufuri ta Najeriya (NITT) da ke Zariya a jihar Kaduna ta kaddamar da gwajin tashin jirage marasa matuka da injiniyoyinta suka…

Cibiyar Koyar da Harkokin Sufuri ta Najeriya (NITT) da ke Zariya a jihar Kaduna ta kaddamar da gwajin tashin jirage marasa matuka da injiniyoyinta suka kera.

An dai gudanar da gwajin ne a hedkwatar hukumar da ke Zariya ranar Juma’a, kuma hakan na nuna irin nisan da cibiyar ta yi wajen kirkira da kuma kawo sauyi a harkokin sufuri na Najeriya.

Shugaban cibiyar, Bayero Salih Farah, wanda gwajin ya gudana a kan idonsa, ya nuna gamsuwarsa da yadda aka kera jiragen, inda ya kera su wata ’yar manuniya ce kan hanyar da suka dauka ta bunkasa fasahar sufuri a cikin gida.

Ya kuma ce, wannan somin tabi ne. muna sa ran ganin lokacin da za mu fara amfabi da irin wadannan jiragen a harkokin sufuri a cikin Najeriya.”

Ga wasu hotunan gwajin jiragen: