✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

CAF ta sanya ranar da za a fara gasar AFCON ta 2025

CAF ya sanyar ranar da za a fara gasar ta AFCON ta 2025.

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF), ta bayyana cewar za a gudanar da Gasar Nahiyar Afirka (AFCON) a watan Disamban 2025 zuwa Janairun 2026.

Caf ta bayyana ƙasar Maroko a matsayin wadda za ta ɗauki nauyin gasar ta 2025 da za fara ranar 21 ga watan Disamban 2025 zuwa ranar 18 ga watan Janairun 2026.

Gasar wadda ƙasashe 24 za su fafata za ta ci karo da lokacin da ake tsaka da murza leda a gasannin a Nahiyar Turai.

Wannan ne karo na farko da za a buga gasar AFCON a lokacin bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara.

Haka kuma, CAF ta sanar da ɗage gasar ƙwallon ƙafar mata ta 2024 zuwa watan Yulin shekara mai zuwa.

Idan ba a manta ba an gudanar da gasar AFCON ta 2024 a ƙasar Ivory Coast, inda ta kai wasan ƙarshe, wanda ta samu nasarar doke Najeriya da ci 2-1.