✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya dawo daga London

Buhari ya dawo Abuja bayan hutun mako biyu don ganin likita a London

Shugaba Muhammadu Buhari ya dawo gida Najeriya bayan hutun mako biyu da ya tafi kasar Birtaniya domin ganin likita a birnin London.

A ranar 30 ga watan Maris Shugaban Kasar ya tashi daga Abuja zuwa London, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce.

Saukar Buhari a Filin Jirgi na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a yammacin Alhamis, tamkar ba-zata ce ga wasu ’yan Najeriya da ke shirin yi masa zanga-zanga a London a ranar Asabar.

A lokacin tafiyar tasa, wasu ’yan Najeriya sun gudanar zanga-zangar adawa da goyon baya a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke London.

Wasu daga cikinsu na zarginsa da nuna halin ko-in-kula game da halin da bangaren lafiya ke ciki a kasar.

Hakan kuma ya zo ne a yayin da ake kai ruwa rana tsakanin gwamnati da likitoci masu barazanar zuwa yajin aiki saboda rashin biyan su hakkokinsu.