✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bom ya kashe jami’an ilimi 2 a Borno

Motar ma'aikatan ilimin ta taka bom din ne a kan babbar hanyar Damboa zuwa Maiduguri, inda wasu da dama suka jikkata

Wasu ma’aikatan lafiya biyu sun rasu, wasu da dama sun jikkata bayan motarsu ta taka bom a kan hanyar Damboa zuwa Maiduguri a Jihar Borno.

Ana zargin mayakan Boko Haram ne suka dasa bom din a wani hari da kungiyar ta kai a kan babbar hanyar a ranar Litinin.

Shaidu sun bayyana cewa, wadanda suka mutun suna zaune ne a gaban motar  jigilar mangoro, kirar Toyota Hiace da ta dauko su daga Damboa zuwa Maiduguri.

Sun kara da cewa tashin bom din ya haifar da sabuwar damuwa game da lafiyar matafiya a kan hanyar.

Wata majiya a karamar hukumar Damboa ta tabbatar da cewa mamatan jami’an Hukumar Ilimi na Karamar Hukumar Damboa ne.

Tuni jami’an tsaro suka killace yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike domin gano ainihin yadda lamarin ya kasance.