Ana ci gaba da aikin ceto bayan mutane da dama sun makale a wani bene mai hawa hudu ya rufa a kansu a Abuja.
Shaidu sun ce mutane da dama ne suka makale a cikin ginin da ke unguwar Gwarimpa a ranar Alhamis, kuma an ciro gawarwaki daga baraguzan ginin.
- An ba da belin alkalan da ake zargi kan bacewar N500m na marayu
- NAJERIYA A YAU: Su wa ke yi wa Tinubu bi ta da kulli?
Kawo yanzu dai, “An ceto mutum shida,” in ji wata darakta a Hukumar Agajin Gaggawa a Kasa (FEMA) Florence Wenegieme, da ake abbaar da faruwar lamarin.
Ta bayyana cewa an garzaya da mutanen da aka ceto zuwa Asibitin Gwarimpa, inda ake jinyar su.