✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bene mai hawa 4 ya rufta a kan mutane a Abuja

Ana ci gaba da aikin ceto bayan mutane da dama sun makale a wani bene mai hawa hudu ya rufa a kansu a Abuja.

Ana ci gaba da aikin ceto bayan mutane da dama sun makale a wani bene mai hawa hudu ya rufa a kansu a Abuja.

Shaidu sun ce mutane da dama ne suka makale a cikin ginin da ke unguwar Gwarimpa a ranar Alhamis, kuma an ciro gawarwaki daga baraguzan ginin.

Kawo yanzu dai, “An ceto mutum shida,” in ji wata darakta a Hukumar Agajin Gaggawa a Kasa (FEMA) Florence Wenegieme, da ake abbaar da faruwar lamarin.

Ta bayyana cewa an garzaya da mutanen da aka ceto zuwa Asibitin Gwarimpa, inda ake jinyar su.