✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Basaraken da ya yi barazanar gayyatar IPOB ya gurfana a kotu

Nwagu ya kara da cewa kungiyar za ta koya wa mutanen jihar hankali.

An gurfanar da wani basaraken kabilar Igbo wanda ya lashi takobin gayyatar kungiyar ta’addanci ta IPOB zuwa a Jihar Legas.

A yayin da yake barazanar gayyatar IPOB domin kare duniyoyin ’yan kabilar Igbo a Legas, Nwagu ya ce kungiyar za ta koya wa mutanen jihar hankali.

Bayan barazanar Frederick Nwagu ga rayuka a dukiyoyin jama’ar jihar ta hanyar amfani da IPOB ne a ranar 1 ga watan Afrilu jami’an hukumar tsaro ta DSS da ’yan sanda suka cafke shi.

Gwamnatin Jihar Legas ta gurfanar da shi a gaban babbar kotun jihar bisa zargin, “yunkurin ta’addanci da halartar taro da nufin daukar nauyin ’yan ta’adda.”

Sai dai Nwagu, wanda shi ne tsohon shugaban ’yan kabilar Igbo  da ke rukunin gidaje na Ajao da ke jihar,  ya musanta zargin.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Y. A Adesanya ya dage sauraron karar zuwa ranar 4 da kuma 5 ga watan Yuni, 2023.