✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Barin Yari daga jihar ya haddasa yawan kashe-kashe a Zamfara

Rohotanni daga jihar Zamfara na bayyana cewa, yawan kashe-kashen da ‘yan fashi da makami suke yi a jihar, sanadiyyar fita da Gwamnan jihar ya yi…

Rohotanni daga jihar Zamfara na bayyana cewa, yawan kashe-kashen da ‘yan fashi da makami suke yi a jihar, sanadiyyar fita da Gwamnan jihar ya yi ne na wasu kwanaki yasa lamarin ya karu.

Sama da mutum 40 aka kashe a cikin mako biyu a sababbin hareharen da ‘yan fashi da makami da barayin shanu suka kai wasu unguwanni da dama a jihar.

A ranar Litinin ne matasa a karamar hukumar Tsafe suka gudanar da zanga-zangar damuwa da yawan kashe-kashen da ake yi a Zamfara.