✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Baje-kolin burgamin Baba

Baje-kolin burgamin Baba Dubu karamin laujen silin girbi Mun karke a zubi Ci-maka mai kumbura tumbi Fafutika aikin ga ka saba Matsaloli tsibi-tsibi Datse  talauci…

Baje-kolin burgamin Baba

Dubu karamin laujen silin girbi

Mun karke a zubi

Ci-maka mai kumbura tumbi

Fafutika aikin ga ka saba

Matsaloli tsibi-tsibi

Datse  talauci da takobi

Sasari a sare da masassabi

Ai maganin masu kinbibi

Kyawun manufa babu munin lakabi

Baba ya bude sabon babi

Gandun na-duke labi-labi

Mu kara doro ya na mai kusunbi

Mu dai tsimayi ranar girbi

kwazo na kawar wa shuka wabi

Samarin kusu sun arce

Dukiyarmu sun kwashe

Lalitarmu sun wawushe

Mai dan boto yau ta kece

Da mun yi kaura in sun zarce

’Yan matan jaba an yi bakace

Ba kama suna sai dai kwatance

Santala-kwaiduwa ta illata tsuntsaye

’Yar’didi kasuwar ajrri tai jaye-jaye

Harr tattalinmu ya balbalce

Turka-turkar tatso tunkuza

An daina hakar kuza

bula bututu har da su man kaza

Ga babban kato kazaza

Rasa kunya mai borin barhaza

An yi Asara-dan-kwabo

Dukiyrmu sun yi mata tabo

kasarmu an yi mata gyambo

Bokokon bobo

Wasu sun karke da kwambo

 A farmaki fari

kamfar marka-marka na haifar da fari

karancin taki na kassara iri

Tohon tunkudowar biri

Ban da yi wa amfani cin birrbiri

Hada-hadar kasuwancin dankoli

Ana sayar da tandun kwalli

Gyara na-mujiya yai walwali

A cire wa fullo haraji da jangali

Kowwa yai aiki da hankali

Kauce wa karafkiyar koriyawa

Gabashin tsakiyar Larabawa

Burtsatsen baza bezar Birtaniyawa

Kandamar kunun Kudancin Amurkawa

Al’amuran sun harari Haurobiyawa

Girkin Girkawa

Tattalin tulun Turawa

Turuwar Turkawa

Sasarin Siriyawa

Jimurdar Jamusawa

karfanfanar kwashe asi

Kamfanin Inda-sisi

Tattalin taro da sisi

A Jihar Lallaga-sisi

Su Lasisi sun samu lasisi

’Yan makaranta

A tsanake tsaf mui bita

Da karfinmu karkaf kwata

Mu farmaki mabarnata

Da masu surutu ratatata

Baje-kolin burgamin Baba

karamin laujen silin madambaci

kasarmu za ta fice daga kunci

Mu dai mu daina tababa

A tarbi baki da tabarmar kaba

Usainin-Babajo

Zaftare harajin hajar Hajjo

A tsahirta wa cinikin gwanjo

Mun ga takun Baba-ojo

Kyakkyawan tambarin bajo

Tiren-taliya madambaci da da gashin balama dari manuniyar sama Baban-burin-huriyya ya baje kolinsu a farfajiyar Majalisar dokokin Haurrobiya, inda kannen Saurayin-kirinki da wakilan rafkiya karkashin jagorancin dogarinsu suka yi kasake don jin batutuwan da ke kunshe a kundin baje ko;lin Hauron shekara ta dubu karamin lauje da sili da tukunyar dambu. Wannan al’amari na nuni da cewa masu fuka-fukin tashi za su daina zabarin baburidon kabu-kabu, su daura damarar tukunyar dambu a wajen fardar garka da gayauna.

Kodayake an ruwaito cewa aikin haskaka Maman-Bala da birjin gada-gadar Ni-na-ja da harkar sufuri za su kwashi kaso mai tsoka, sai mu yi fatan ganin an himmatu ka’in da na’in rani da kaka don cimmma manufofin da ke kunshe cikin kundi.

Haurrobiyawa ya kamata mu tallafa wa Baba wajen aiwatar da mangartan tsare-tsare ta yadda zai ji dadin aiwatar da baje-kolin Hauron shekara mai karatowa cikin gaugawa ba tare da gigiwa ba.Takun sawun giwa ya zarta na yanyawa ba wani yawa, ballantana a yi ta kokowa.

Matukar ana so a cimmma nasara kada a yi asara, to sai Baba ya fara da haramtawa wa gwamnoninmu WAWAR WADAkAR WAUTA, musamman in ya sake jinka musu Belin-auta, da suke juya akalarsa ya zama Billen-wauta, har ta kai ganin ba a yi sa’a ba, a karke da balbalin wuta. Kuma a himmatu wajen karkata akalar dogaron da albarkatun man tunkuza, don kauce wa turka-turkar tunkuza, musamman bula bututu da takun saka rututu.

Abin da ya sa muka kira baje-kolin Hauro da burgamin Baba, domin ta haka ne kawai za a kange shi daga daga farmaki samarin kusu da ’yan matan jaba da gafiya, masu kwasar gararumar gyaran jar miya. Kodayake ma Iro Mugun madambaci ba zai yi musu sassauci ba.

Lallai mu yi kishi ban da kisisina da yi wa kasa kisan mummmuke, kada kowa ya noke, mu fito mu daina sake-sake, har a cimma manufar gina kasa ta hanyar aiwatar da baje-kolin Hauron shekara ta dubu karamin lauje da sili da madambaci, ko al’ummar kasarmu sun fice daga kunci. Tuni dai an yi maganin ’yan ku ci mu ci, ballantan masu shaci-fadi da suka kwaso duniya da fadi, wadanda ke haifar wa mutane radadi.