Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, ya bayyana takaicinsa kan sake durkushewar tattalin arzkin Najeriya da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta sanar.
A ranar Asabar ce hukumar ta fitar da sabon rahoton da ke cewa tattalin arzikin kasar ya sake durkushewa.
- DAF ta kashe mutum 4 a wani hadari
- Mahara sun kashe shugaban dalibai a Kaduna
- An kama mutanen da ‘suka ci balangun gawar ‘Yan sanda’
“Na kadu matuka da samun rahoton sake karyewar tattalin arzikin a karo na biyu cikin shekara biyar”, inji Atiku ta shafinsa na Twitter.
NBS ta ce tattalin arzikin Najeriya ya ragu da kaso 3.62% a tsakanin watan Yuli zuwa Satumban 2020.
Karyewar tattalin arzikin na nufin yiwuwar kara tabarbarewar al’amuran rayuwa da hauhawar farashin kayan masarufi.
Sauran sun hada da karancin kudin biyan bukatu, rashin ayyukan yi da durkushewar masana’antu.