✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

ASUU ta yi barazanar tsunduma yajin aiki kan ƙarancin albashi

ASUU ta koka kan yadda aka waiwayi albashin wasu ma'aikata amma ban da na mambobinta.

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU),  ta yi barazanar shiga yajin aiki idan Gwamnatin Tarayya ta gaza duba albashin mambobinta tare da samar da isassun kuɗaɗen Jami’o’i.

A yayin wani taron manema labarai a Uyo da aka yi a ranar Litinin, Kwamared Happiness Uduk, Shugabar ASUU ta shiyyar Kalaba, ta bayyana damuwarta a madadin shugabannin jami’o’i daban-daban.

Uduk, ta ce tun bayan shekara 15 ba a sake duba albashin malaman jami’o’i ba, duk da wasu sassa kamar majalisa, ‘yan sanda da sojoji da kuma ɓangaren shari’a an sake tattaunawa kan albashinsu sau da yawa.

Ta kuma koka da cewa tun farkon fitar da Naira biliyan 200 daga cikin Naira tiriliyan 1.3 da Gwamnatin Tarayya ta yi alƙawarin farfaɗo da jami’o’in gwamnati a 2013, ba a sake fitar da wasu kuɗaɗe ba.

Wannan ya sha bamban da yadda gwamnati ke kashe Naira biliyan 90 a aikin hajji tare da yin watsi da fannin ilimi, in ji ta.

A halin da ake ciki, ASUU reshen Abuja ta nuna rashin jin daɗinta kan yadda ake ci gaba da biyan albashin mambobin kungiyar ta hanyar tsarin biyan albashi na  IPPIS.

Ta koka duk da umarnin da Gwamnatin Tarayya ta bayar na cire manyan makarantu daga tsarin na watanni huɗu da suka gabata.

Shugaban Ƙungiyar ASUU na shiyyar Abuja, Salahu Mohammed Lawal ne, ya bayyana haka a ranar Litinin yayin wani taron manema labarai a Abuja.

Shiyyar ta ƙunshi Jami’ar Abuja; Jami’ar Tarayya, Lafiya; Jami’ar Fasaha ta Tarayya, Minna; Jami’ar Ibrahim Badamasi, Lapai, Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi.