Kocin kulob din Arsenal da ke Ingila Arsene Wenger ya bayyana cewa akwai yiwuwar ya dauke dan kwallon Najeriya Joseph Yobo a watan Janairun badi idan aka bude kasuwar saye da sayar da ’yan kwallo.
Kamar yadda kafar sardarwa ta Daily Mail ta kalato, baya ga Joseph Yobo, kulob din yana zawarcin Diego Lugano tsohon dan kwallon West Brom a watan na Janairu.
Yobo dai ya taba yi wa kulob din Eberton na Ingila wasa kafin ya koma Turkiyya don cigaba da yin kwallo.
Arsenal ta fara zawarcin Joseph Yobo 2
Kocin kulob din Arsenal da ke Ingila Arsene Wenger ya bayyana cewa akwai yiwuwar ya dauke dan kwallon Najeriya Joseph Yobo a watan Janairun badi…