Rahotanni da ke fitowa daga Ingila sun nuna kulob din Arsenal ya fara tunanin maye gurbin kocinsa na yanzu Arsene Wenger a karshen kakar wasa ta bana.
Kulob din ya fara wannan yunkuri ne bayan kulob din Manchester City ya lallasa na Arsenal da ci 3-0 a kofin Carabao a ranar Lahadin da ta wuce da hakan ta sa mahukunta kulob din suka fara yunkurin rabuwa da shi.
A bara ne kulob din ya sabunta kwantaragin Wenger da shekara biyu bayan ya yi kokarin lashe kofin kalubale (FA) amma a bana sai kulob din ya samu koma-baya.
A halin yanzu kulob din Arsenal yana sa rai ne a kofin Europa kuma akwai yiwuwar idan ya yi sake to za a iya yi masa sakiyar da babu ruwa a kakar wasa ta bana inda zai tashi hannu rabbana.
Sai dai ana rade-radin idan kulob din ya kori Wenger to zai maye gurbinsa ne da tsohon kocin Liberpool Brenden Rodgers da yanzu haka yake horar da kulob din Celtic.