✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ana zargin Hajiyar Najeriya ta kashe kanta a Saudiyya

Alhazan Jihar Kwara biyu sun rasa ransa a birnin Madina

Ana fargaba cewa wata hajiyar Najeriya daga jihar Kwara ta kashe kanta a birnin Madina da ke kasar Saudiyya.

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kwara, ta sanar cewa hajiyar ta yi ajalin kanta ne ta hanyar fadowa daga saman rufin masaukibta da ke Madina.

Hukumar ta ce hajiyar itace mutum ta biyu cikin alhazan jihar da suka rasu a Madina a bana.

Ta kara da cewa wani alhajin jihar mai suna Saliu Mohammed, ya rasu sakamakon rashin lafiya a Madina.

Alhaji Saliyo ya rasu ne a yayin da ake jinyar shi a sashin kula da lafiya na wani asibitin gwamnati da ke Madina.

Hukumar alhaza ta cikin wata sanarwa cewa “wadannan abubuwa masu ban tausayi be, amma tana mika wuya ga kaddara da sanin Allah a cikin dukkan al’amura.”

A cikin wata sanarwa da shugaban hukumar Abdulsalam Abdulkadir ya fitar, ya mika sakon ta’aziyya ga iyalansu, inda ya roki Allah Ya jikan wadanda suka rasu Ya kuma gafarta musu.