✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An sako daliban jami’ar ABU 3 da aka yi garkuwa da su

An kubutar da daliban jami’ar Ahmadu Bello(ABU) Zariya da aka yi garkuwa da su a hanyar Abuja zuwa Kaduna ranar Litinin da yamma. Daliban da…

An kubutar da daliban jami’ar Ahmadu Bello(ABU) Zariya da aka yi garkuwa da su a hanyar Abuja zuwa Kaduna ranar Litinin da yamma. Daliban da aka yi garkuwan da su ne: Fatima Jalingo, Maryam Bello da Umar Sagir, dukkan suna ajin karshe a jami’ar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da sakin daliban.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Kaduna DSP Yakubu Sabo, ne ya tabbatar da hakan a jiya Laraba da Yamma, inda ya ce daliban jami’ar na cikin wadanda suka fada cikin tarkon masu garkuwa da mutanen ranar 26 ga Agusta 2019 a hanyar Kaduna zuwa Abuja.

“Dama suke nan wadanda ba a sako su ba a yanzu haka sun koma gaban iyayen su.” In ji DSP Yakubu.