✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An rufe Jami’ar Maiduguri saboda ambaliya

An rufe Jami'ar Maiduguri nan take

Jami’ar Maiduguri ta dakatar da darussa sauran harkokinta nan take sakamakon ambaliyar da ta mamaye birnin.

Sanarwar da Magatakardan jami’ar, Ahmed A. Lawan ya fitar ranar Talata ta kara da cewa an dakatar da karatu da sauran ayyuka har zuwa lokacin da za a fitar da sanarwa ta gaba.

Ya bayyana cewa yin hakan ya zama tilas domin kare rayukan dalibai da malamai da sauran ma’aikata da kuma nazarin halin da ake ciki.

Aminiya ta ruwaito yadda ’yan Kasuwar Monday Market da kasuwannin Maiduguri suka tafka mummunar asara sakamakon ambaliya.

Dalilin Ambaliyar Maiduguri

Ambaliyar Maiduguri ta samo asali ne daga ruwan sama kamar da bakin kwarya ta da aka tafka na tsawon kwanaki.

Daga bisani, lamarin ya haddasa fashewar Madatsar Ruwa ta Alau mai nisan kilomita 10 daga garin.

ِA cikin dare ruwan ya fara mamayw unguwanni, inda kafin wayewar gari yawancin unugwannin Maiduguri suna cikin ruwa, a wani yanayi da shekaru 30 ke nan rabon da ga irinsa a garin.

Ranar Litinin da tsakar dare ambaliyar ta yunkuro, inda ta raba dubban mazauna unguwannin Post Office, Gwange, Moromoro, Gadar Customs, Gidan Zoo, Bulabullin, Maidoki  Roundabout, Jami’ar Maiduguri, Cocin Saint Patrick da sauaransu da muhallansu.

Wani dan kasuwa ya ce, “Duk shagunan da ke Monday Market da Post Office ruwa ya shanye su.”

Wakilinmu a garin Maidurugi ya zagaya garin, inda ya iske ’yan kasuwar Monday Market suna lissafin irin asarar da suka yi sakamkon ibtila’in.

Wasu daga cikinsu sun nuna matukar kaduwarsu da kuma tunanin yiyuwar maye gurbin abin da suka rasa a ambaliyar.

Wani mai sayar da sukari da fulawa a kasuwar, Muhammad Bulama, ya ce ambaliyar ta shanye kasuwar gaba daya.

“Duk shagunanmu da ke kallon gidan Marigayi Alhaji Mai Sugar sun yi ambaliya, sukari da fulawa da shinkafa da kayan girki na miliyoyin Naira sun lalace.

“A sa mu a add’ua! Buhunan kayan abinci irin su sukari da shinkafa da gishiri da taliya da sauransu duk sun jike sun narke,” in ji shi.

Wakilinmu ya lura yawan ruwan da ke ambaliyar yana kara kaurwa inda yake kara shiga wasu unugwanni.

Hakazalika ambaliya ta mamaye Gidan Zoo na Kyarimi ta wuce da namun dajin da ke ciki, inda a halin da ake ciki namun dajin suke neman mafaka.

Wani mazaunin yankin ya ce, “yanzu haka mun fice daga unugwar saboda gudun hari daga namun daji da kwarin da ke gidan zoo.

Rundunar ’yan sanda a Jihar Borno ta bukaci jama’a da su kaurace wa yankunan da aka samu ambabaliya zuwa wasu wurare masu aminci.