✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kuɓutar da yaro daga hannun masu garkuwa da mutane a Yobe

An cafke jagoran masu garkuwar yayin da sauran suka tsere.

Rundunar ‘yan sanda a Jihar Yobe ta kuɓutar da wani ƙaramin yaro mai suna Adamu Sani daga hannun masu garkuwa da mutane.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Dungus Abdulkareem ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe.

Ya ce jami’an ‘yan sanda hedikwatar da ke Gujba ne suka kuɓutar da yaron tare da kama jagoran masu garkuwar.

Bayanai sun ce, lamarin ya faru ne a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kutsa cikin ƙauyen Bungai na garin Buni Yadi da ke Ƙaramar Hukumar Gujba.

DSP Dungus ya ce maharan sun riƙa harbi da baka da kibiya da kuma bindiga, lamarin da ya ba su damar yi wa mazauna yankin barazana tare da awon gaba da yaron mai shekara uku.

DSP Dungus ya ce a ci gaba da gudanar da ayyukan leken asiri tare da hadin gwiwar ’yan banga, an gano maboyar masu garkuwa da mutane a cikin garin Buni Yadi, inda suka fatattake su, sannan suka kama shugabansu mai suna Yau Usman tare da yaron hannunsa.

A yayin da sauran masu garkuwar suka tsere, an garzaya da yaron da aka ceto zuwa asibiti domin duba lafiyarsa.