✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama masu kwacen waya 26 a Jigawa

Rundunar ta ce ta kama masu laifin ne bayan wani samame da ta kai daban-daban a jihar.

Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama mutum 26 da ake zargi da aikata kwacen wayoyi da kuma shan muggan kwayoyi.

Kakakin rundunar, DSP Lawan Shiisu, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Dutse.

Ya ce kamen ya biyo bayan wasu jerin samame da suka kai a tsakanin ranar 18 zuwa 19 ga watan Disamba, a kananan hukumomi hudu na jihar.

Kakakin ya ce jami’an rundunar sun kama wani matashi kan zargin satar waya da kuma sata kudi Naira 10,000 a garin Babura da ke Karamar Hukumar Babura.

Kazalika, sun kama wasu mutum biyu kan zargin laifin satar kwamfutoci shida da babur a Hadejia.