✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama mahaifiya da ‘yarta kan zargin kisan malamar makaranta

‘Yan sanda sun kama wata mata mai matsakaicin shekaru da ’yarta kan zargin dukan wata malamar makaranta har suka kashe ta a jihar Anambara. Marigayiyar…

‘Yan sanda sun kama wata mata mai matsakaicin shekaru da ’yarta kan zargin dukan wata malamar makaranta har suka kashe ta a jihar Anambara.
Marigayiyar mai suna Rita, wacce ke koyar da harshen Igbo a makarantar sakandire mai suna Starlight da ke kauyen Ogidi da ke garin Idemili ta Arewa da ke cikin jihar ta yanke jiki ta fadi bayan da matar da ’yarta da wani mutum suka rika dukanta da tsintsiya.