Rundunar sojojin Najeriya ta yi nasarar kama wani kasurgumin dillalin muggan makamai da yake kaiwa ‘yan bindigar da suka addabi hanyar Kaduna zuwa Abuja wanda suke takura matafiya a hanyar.
Rundunar sojojin da ke da cibiya a Kaduna sun yi nasarar kama dillalin mai suna Alhaji Shehu, wanda gidansa ya ke unguwar Sabogaya, cikin Karamar Hukumar Chikun a jihar Kaduna.
An kuma yi nasarar kama wasu mutum biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, suna kokarin karbar hayar bindigogin AK47 don gudanar hare-hare.
Mataimakin Diraktan sashin hulda da jama’a na rundunar ta1 Division, Kanal Ezindu Idimah ya tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ya fitar a Kaduna. Ya ce, an kama dillalin bindigogin a ranar Asabar dauke da bindigogin kirar AK47 guda 6.