✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Amurka za ta inganta ƙarfin Intanet a Afirka

Hankali ya karkata kan Afirka a matsayin wacce makomar ci gaba na duniya ya dogara da ita.

Gwamnatin Amurka ta sanar da shirinta na inganta karfin Intanet a nahiyar Afirka zuwa kashi 80 ciki 100 nan da shekarar 2030.

Amurka za ta inganta ƙarfin samun shiga yanar gizo daga kaso 40 cikin 100 da ake da shi yanzu a nahiyar.

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwar da Mataimakiyar Shugabar Amurka, Kamala Harris ta yi a ranar Juma’a.

Sanarwar da ta yi na zuwa ne bayan shekara guda da ziyarar da ta kai nahiyar Afirka, a daidai lokacin da suka zanta da Shugaban Kenya, William Ruto a birnin Washington.

Wannan na daga cikin manufofin Amurkar na karfafa hulɗar tattalin arziki da nahiyar Afirka, nahiyar da hankali ya karkata kanta a matsayin wacce makomar ci gaba na duniya ya dogara da ita.

Bankin bunkasa kasashen Afirka da ma wasu ƙungiyoyi sun ƙara himma wajen inganta fannin sadarwar zamani, inda za a fara da samar da Intanet mai ƙarfi ga manoma a ƙasashen Kenya da Tanzaniya da ma Najeriya a tashin farko kafin abin ya kai ga sauran ƙasashen na nahiyar.

A bara ce dai Kammala Harris ta ziyarci kasashen Ghana, Tanzaniya da Zambiya, inda ta bayyana ƙudirin Amurka na inganta harkokin intanet da ci gaban fasahar zamani a nahiyyar.