Tsohon dan kwallon Najeriya Super Eagles, Emmanuel Amunike ya samu nasarar hayewa da kasar Tanzaniya zuwa gasar cin Kofin Afirka na bana wanda za a yi a watan Yunin a karon bayan shekara 39.
Rabon da kasar ta halarci gasar cin Kofin Afirka tun a 1980.
Koci Amunike ya samu wannan nasara ce bayan Tanzaniya ta lallasa kasar Uganda da ci 3-0 a ranar Litinin da ta wuce wanda ya ba ta damar hayewa zuwa gasar da za ta gudana a kasar Masar..
Tanzaniya dai ta lallasa Uganda ne da ci 3-0 a filin wasanta na Dar es Salaam. ’Yan kwallon Tanzaniya Simon Msuwa da Erasto Nyoni da kuma Aggrey Morris ne suka zura kwallayen da ya ba kasar tasu nasara.
A watan Agustan 2018 ne Emmanuel Amunike ya sanya hannu a kwantaragin shekara biyu da kasar Tanzaniya don horar da kungiyar kwallon kafa ta kasar. Ga shi ya ba marada kunya inda ya haye da kasar zuwa gasar cin Kofin Afirka a karon farko cikin shekara 39.
Amunike yana daga cikin ’yan kwallon Super Eagles da suka samu nasarar lashe Kofin Afirka a 1994 kuma yana daga cikin wadanda suka lashe lambar zinare a wasan kwallon kafa a gasar Olamfik da aka yi a Atlanta a 1996.
Ya horar da kungiyar kwallon kafa ta Najeriya a matakin U-17 da U-21 da kuma U-23 a lokuta daban-daban kafin ya tafi Tanzaniya don horar da kungiyar kwallon kafa ta kasar.