✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ambaliya: Mazauna Legas sun makale bayan ruwa kamar da bakin kwarya

Ruwan saman na sama da sa'o'i shida an fara shi ne da misalin karfe 6 na safe, kuma ambaliyar ta shanye yawancin tituna da gadoji…

Mutane da dama sun makale a gidajensu bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya haddasa ambaliya a Karamar Hukumar Alimosho da ke Legas.

Ruwan saman na sama da sa’o’i shida an fara shi ne da misalin karfe 6 na safe, kuma ambaliyar ta shanye yawancin tituna da gadoji da ke birnin.

Hakan ya tsaiko ga zirga-zirgar ababen hawa, a yayin da motocin haya ke guje wa wuraren da abin ya shafa.

Unguwannin da abin ya fi shafa sun hada da Abule-Egba, Command, Agege da unguwar Egbeda.

Masu aikin ceto daga hukumomin jihar da na gwamnatin tarayya suna ci gaba da aiki domin ceto wadanda suka makale.

Ko’odinetan Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) a shiyyar Kudu maso Yamma, Ibrahim Farinloye, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A wani sako da ya aike ta WhatsApp, ya shawarci mazauna yankin Command da su bi wasu hanyoyin daban, idan za su fita, saboda ambaliyar ta mamaye gadar.