Wannan nasarar da Najeriya ta samu ya sa ta zama ta farko da ta kai zagayen gaba a gasar cin kofin Nahiyar Afirka ‘Afcon 2019’ da ake yi a kasar Masar.
Super Eagles ta yi nasarar ne bayan doke Guinea da ci daya mai ban haushi a wasa na biyu na rukuni na biyu da suka fafata a Alexandria.
Najeriya ta ci kwallon ne ta hannun dan wasanta Kenneth Omeruo.