✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Aso Rock

Wannan dai na zuwa ne bayan jawabin da Tinubu ya yi wa 'yan ƙasar a ranar Lahadi.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ɗage taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), inda ya gana da shugabannin tsaro a Aso Rock.

Ministocin da suka isa wajen taron an hange su suna barin a Fadar Shugaban Ƙasa kimanin ƙarfe 12 na rana.

Kaɗan daga cikin ministoci ne suka isa lokacin da aka ɗage taron.

Aminiya ta samu labarin cewa ɗage taron ba zai rasa nasaba da wani taro kan sha’anin tsaro da Shugaba Bola Tinubu ke jagoranta a fadar shugaban ƙasa.

Ko da yake ba a bayyana ajandar taron ba, ana tsammanin majalisar za ta tattauna kan zanga-zangar da ake yi a yanzu da kuma yanke shawarar matakin da ya dace a ɗauka.

Taron ya biyo bayan jawabin da Shugaba Tinubu ya yi wa ’yan Najeriya da safiyar ranar Lahadi, inda ya buƙaci masu zanga-zanga su buɗe tattaunawa domin nemo mafita.