Shugaban kungiyar kwadago NLC ta Najeriya Ayuba Wabba ya ce, duk gwamnnonin da suka ki amincewa da yarjejeniya da aka yi na biyan albashi mafi karanci, zai rasa kuri’un ma’aikatan jiharsa a zaben mai zuwa.
Shugaban ya bukaci ma’aikatan su gagauta daukan matakan yin waje da gwamnan da ya ki amincewa da sharuddan kungiyar kwadago.