✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za mu bai wa masu zuba jari cikakken goyon baya – Ganduje

Gwamnan Jihar Kano ya ce gwamnatinsa za ta bai wa masu zuba jarin kasashen ketare cikakken goyon baya domin su zuba jari domin bunkasa kasuwanci…

Gwamnan Jihar Kano ya ce gwamnatinsa za ta bai wa masu zuba jarin kasashen ketare cikakken goyon baya domin su zuba jari domin bunkasa kasuwanci a jihar.
Gwamnan Jihar Dokta Abdullahi Ganduje  ya  yi wannan albishir din ne lokacin bikin bude Kasuwar Baje Koli karo na  38 a jihar da aka yi ranar Lahadin da ta gabata, inda ya ce idan aka samu masu zuba jari cikin harkokin kasuwanci  ko shakka babu za’a samu karuwar arziki da  bunkasar masana’antu kamar yadda ake gani a kasashen duniya.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin kwamishinan ma’aikatar kasuwanci ta jihar, Alhaji Rabi’u Bako, ya ce jihar tana da albarkatun kasa da ake bukata domin sarrafawa a kamfanoni da masana’antu, don haka akwai bukatar samun masu zuba jari ta yadda za’a amfani wadannan albarkatu sosai.
Shugaban Majalisar Bunkasa Kasuwanci da  Masana’antu da Ma’adinai da kuma Aikin Gona wato (KACCIMA),  Alhaji Umar dan Sulaika ya bayyana cewa ana gudanar da baje koli ne domin a kulla wasu huldar kasuwanci.