✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a binne gawarwaki 60 da ba a gano ’yan uwansu ba a Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba a makabartar Tudun Wada

Gwamnatin Jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba.

Sashin Lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu zai dauki gawawwakin don binnewa a a Makabartar Layin Bashama da ke unguwar Tudun Wada.

Mataimakiyar Sashin lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta kudu- Asmau Saidu Adamu ta sanar cewa za a binne gawarwakin ne a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba da muke ciki.

“Za a dauko gawarwakin ne daga Asibitin Gwamna Awan zuwa Makabartar Bashama Road, karkashin jagorancin Kwamishinar Lafiya ta Jihar Kaduna, Umma K Ahmed da Shugaban Asibitin Gwamna Awan, Dokta Gebriel Brown,” inji ta.