Wani Kamfanin jarida na birnin Landan mai suna African voice ya zabi taurarin kannywood guda bakwai domin ba su lambar yabo dangane da qwazon da suka nuna a masana’antar ta kannywood. Bikin bada lambar yabon za a yishi ne a ranar hudu ga watan Nuwamba , 2017.
Taurarin da zasu amshi lambar yabon sun hada da Nafisa Abdullahi, Hafsat Ahmed, Halima Atete, Ramadan Booth, Sani Ahmad Yaro, Kamal Alkali da Hamisu Lamido Iyantama.
Lambar yabon zai kasance a vangarori uku: ‘yan wasa, bada umarni da kuma shiryawa.