Asisat Oshoala ta sake lashe gasar gwarzuwar ‘yar kwallon Afirka karo uku bayan ta lashe gasar a shekarar 2014 da 2016.
Asisat, ‘yar shekara 23 a rayuwa ta bugawa kungiyar Arsenal Ladies da Liverpool Ladies kafin ta koma Kasar China inda take ci gaba da taka leda.
Ta taimakawa kungiyar Dalian Quanjian lashe gasa biyu a kakan bara, inda ta zura kwallaye 19.