✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan Boko Haram 119 Sun Mika Wuya Cikin wata 1 —MNJTF

Wani kwamandan Boko Haram Adamu Muhammad da wasu mayakansa biyar sun mika wuya ga sojojin a Monguno da ke Jihar Borno a ranar Alhamis. Babban…

Wani kwamandan Boko Haram Adamu Muhammad da wasu mayakansa biyar sun mika wuya ga sojojin a Monguno da ke Jihar Borno a ranar Alhamis.

Babban jami’in yada labaran rundunar sojin na N’djamena-Chad, Laftanar Kanar Abubakar Abdullahi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Maiduguri ranar Juma’a.

Ya bayyana cewa wadanda suka mika wuya sun kawo adadin ’yan ta’addan da suka tuba tun bayan a wata daya da ya gabata zuwa 119.

A cewarsa, ’yan ta’addan sun tsere daga maboyar kungiyar ISWAP a Jubillaram, da ke Kudancin tafkin Chadi.

Ya ce, “Adamu, mai shekaru 22, ya kai hare-haren ta’addanci da dama, ya kuma yi yawo sosai a yankunan da ake fama da ta’addanci a jihar Borno.

“A lokacin da suka mika wuya, sun mika harsashi na musamman guda 11 na 7.62mm da harsashin harbo jirgin sama guda daya”

MNJTF ta yi kira ga sauran ’yan ta’adda da su yi koyi da waɗanda suka mika wuya, su ajiye makamansu, su rungumi zaman lafiya.

Ya ce, suna jaddada aniyarsu ta tabbatar da ingantaccen wurin rayuwa a yankin tafkin Chadi.