Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa wasu ‘yan bindiga sun kaiwa kauyen Kware hari inda suka kashe mutane akalla mutum 30 a karamar hukumar Shinkafi.
An kai harin ne a tsakiyar daren ranar Lahadi, bayan kashe mutanen da ‘yan bindigar suka yi sun kone gidajen mutane da dama.
Rahotan bayyana cewa, an birne wadanda aka kashe a kauyen.