Rundunar ’Yan Sandan Jihar Legas ta tabbatar da cewa wasu ’yan bindiga sun kashe mutum uku a rukunin gidajen Gowon da ke unguwar Ipaja a jihar.
Kakakin rundunar, SP Benjamin Hundeyin, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) a ranar Alhamis cewa ce lamarin ya faru ne a ranar Laraba da misalin karfe 11:35 na dare.
- Azumi: Gwamnatin Kano ta bai wa dalibai hutun sati 3
- Jirgin ruwa dauke da mutane ya yi hatsari a tsakiyar kogi a Bayelsa
Ya ce, ofishin ’yan sanda na yankin ya samu kiran gaggauwa cewar wasu ’yan bindiga sun harbe wasu mutane a cikin wani gida.
Wani ganau ya ce nan da nan maharan suka bar rukunin gidajen bayan harbe mutanen.
Hundeyin ya ce an garzaya da wadanda abin ya shafa zuwa babban asibitin Igando.
“Bayanan da ’yan sanda suka samu sun nuna cewa ’yan uwan biyu daga cikin wadanda suka mutu sun dauke su.
“Wani mutum da ya tsira daga harin, Doba Ngoze, yanzu haka yana kwance a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Legas, da ke Idi-Araba,” in ji shi.
Kakakin ya ce tuni aka fara gudanar da bincike kan lamarin.