✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAJERIYA A YAU: Yadda Mabaratan Zamani Ke Neman Hana Bayar Da Sadaka

Yadda lafiyayyu mutane da ke barar zamani suke karuwa fiye da nakasassu da almajirai. 

More Podcasts

Lafiyayyun mutane da ba nakasassu ko ’yan makarantar allo ba, da suka rungumi dabi’ar bara sai kara karuwa suke.

Lamarin ya kai da wuya mutum ya fito ya koma gida ba tare da wani ya yi masa ba-zata ya roke shi kudi ko abin ci ba.

Yawancin masu irin wannan rokon sukan fito ne tsaf-tsaf kamar wasu ma’aikata ko ’yan kasuwa.

Shin yaya jama’a ke kallon wannan dabi’a da ta zama ruwan dare?

Shirin Najeriya A Yau na wanna lokaci na tafe da karin bayani.

Domin sauke shirin kai tsaye, latsa nan