✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda jiragen soji suka ragargaji ’yan bindiga a dajin Kaduna

Jiragen sojin sun ragargaza maboyar yan bindigar a dazukan Igabi da Giwa

Jiragen Rundunar Sojin sama ta Najeriya sun ragargaza ’yan bindiga da dama a dazukan kananan hukummin Giwa da Igaba a Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar, AVM Edward Gabkwet ya ce a ranar Juma’a jiragen yakin suka tarwatsa maboyar wani dan bindiga mai suna Alhaji Layi a yankin Kufan Shantu da ke Karamar Hukumar Giwa.

Jami’in ta ci gaba da cewa a yayin harin, jiragen sun kuma ragargaza ma’adanar kayan amfanin ’yan ta’addan.

Jiragen sun kai makamancin harin a Dajin Malum na Karamar Hukumar Igabi, inda “suka hango ’yan ta’addan sunan kai-komo a sansaninsu, suka tarwatsa shi, suka aika su barzahu.

Edward Gabkwet ya jiragen sojin sun kai hare-haren ne a ci gaba da aikin da suke yi na murkushe ’yan ta’adda a yankin Arewa masu yamma.

Sanarwar da ya sanya wa hannu a ranar Lahadi ta ce, duk da kalubalen da suke fuskanta, sojoji na samun nasara a aikin kakkabe ’yan bindiga a yankinn.

(NAN)