✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya

Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin…

Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na karamar hukumar Mokwa a jihar Neja a ranar Laraba.

Ambaliyar, wacce ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka a daren na Laraba, ta kuma lalata dukiyoyi da dama, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman wasu mutanen da suka bace.

Garin Mokwa dai ya shahara da zama wani zango na direbobin manyan motoci, wanda hakan ya sa garin ya zama daya daga cikin mafiya hada-hadar mutane a jihar ta Neja.

Aminiya ta gano cewa akasarin wadanda iftila’in ya fi shafa mata ne da kananan yara.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta tabbatar da mutuwar mutum 21, amma mutanen yankin sun ce wadanda suka mutu za su iya haura 60.

Daga cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar har da wata dalibar Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jihar Neja mai suna Binta, wacce ta je garin na Mokwa domin yin hutu, kuma tuni har an samo gawarta.

Wata ’yar yankin mai suna Hajiya Hassana Mokwa, ta shaida wa wakilinmu cewa akalla danginta 12 zuwa 13 ne suka rasu a ambaliyar, wanda kawai ya saura kuma yanzu haka yana can a kwance a asibiti ranga-ranga.

Ta kuma ce akwai wasu daliban makarantar Alkur’ani mallakin dan uwanta da su ma suka rasa ransu.

“Akwai almajirai da dama a makarantar Alkur’anin dan uwana da su ma suka rasu. Babu wanda ya saura da rai a cikin gidan, gaba daya gidan nitsewa ya yi. Idan ka je wajen yanzu, ba za ka taba tinanin ma an taba yin gini a wajen ba,” in ji Hajiya Hassana.