✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano

Ya soka wa abokinsa wuƙa a lokacin da faɗa ya kaure tsakaninsu a kan wata hular sanyi

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke hukuncin ratayewa ga wani mutum da ta samu da laifin kashe abokinsa saboda hula.

Kotun da ke zamanta a kan titin Miller ta yanke wa mutumin mai suna Adamu Isma’ila Arzai hukuncin ne bayan an gurfanar da shi kan zargin soka wa abokinsa mai suna Auwal Shehu Kabara wuƙa a lokacin da suke faɗa.

A shekarar 2016 ne faɗa ya kaure tsakanin abokan biyu a kan wata hular sanyi a lokacin da suka yi wata tafiyar fatauci a Jihar Bauchi.

A yayin zaman kotun, mai gabatar da ƙara, Wahida Isma’il, ta gabatar da shaidu biyar, shi kuma wanda ake tuhuma ya kare kansa.

Bayan sauraron duka bangarorin, alƙalin kotun, Mai Shari’a Muhammad Musa Karaye, ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun kawo gamsassun hujjojin da ke tabbatar da cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin.

Daga nan kuma ya yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya.