An tabbatar da mutuwar mutum biyu sanadiyyar tangardar wutar lantarki a mahadar Dadin Kowa da ke Jos ta Kudu a jihar Filato.
Majiyarmu ta gano cewa, wadanda suka rasun matasa ne masu aikin gini da ke ginin sabon bankin United Bank for Africa (UBA), da ake ginawa a unguwar Dadin Kowa lokacin da hadarin ya faru.
Hadarin wutar lantarkin ya rutsa da matasa uku ne biyu daga ciki suka rasu dayan kuwa jinya a asibiti.