✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

WAEC za ta fitar da sakamakon SSCE na 2020 a makon gobe

WAEC ta dage ranar fitar da sakamakon jarabawar sakandare na 2020

Hukumar Shirya Jarabawa ta Yammacin Afirkta (WAEC) ta dage ranar fitar da sakamakon jarabawarta na kammala sakandare da aka gudanar bana zuwa mako mai zuwa.

A ranar Laraba 28 ga Oktoboa ya kamata WAEC ta fitar da sakamakon jarabawar amma ta ce ta dage saboda rikici da kone-konen da aka yi a boren #EndSARS a sassan Najeriya.

“A yau Hukumar ta shirya fitar da sakamakon jarabawar amma dokar hana fita da aka sanya a makon jiya ya sa aka dage fitar da sakamakon zuwa makon gobe. Nan gaba za a sanar da ainihin ranar”, inji sanarwar da WAEC ta wallafa a shafinta na Twitter.

Jami’in Hulda ja Jama’a na Ofishin Hukumar a Najeriya, Demianus Ojijeogu, ya tabbatar da hakan.

Idan ba a manta ba bullar annobar COVID-19 da dokar kulle da aka sanya domin dakile yaduwarta ta sanya an daga gudanar da jarabawar a Najeriya da wasu kasashe.

A baya an saba gudanar da jarabawar ne tsakanin watan Mayu da Yuni, amma bullar a annobar ta sa a 2020 aka gudanar a watan Agusta.