✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

WAEC ta sanar da ranar fara jarrabawar WASSCE ta 2021

Za a fara jarrabawar ne ranar Litinin, 16 ga watan Agustan 2021.

Hukumar Shirya Jarrabawar ta Afirka ta Yamma (WAEC) ta sanar da ranar Litinin, 16 ga watan Agustan 2021 a matsayin ranar da za a fara rubuta jarrabawar kammala sakandire (WASSCE).

Babban jami’in hukumar a Najeriya, Mista Patrick Areghan ne ya sanar da haka a Legas ranar Talata.

A cewar sanarwar, “La’akari da jadawalin da aka amince da shi na kasa da kasa, jarrabawar WASCCE ta shekarar 2021 a dukkan yankin da ake rubutata za ta gudana daga ranar Litinin 16 ga watan Agusta zuwa Juma’a, takwas ga watan Oktoban 2021.

“To sai dai a Najeriya, za a kammala jarrabawar ne ranar 30 ga watan Satumban 2021, bayan an shafe makonni bakwai kenan ana yinta,” inji sanarwar.

A baya dai, akan rubuta jarrabawar ne a tsakanin watannin Afrilu da Mayun kowacce shekara, in ban da a bana da aka sami tsaiko sakamakon yadda annobar COVID-19 ta kawo dagula lamura.