✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Uwargidan Sanata Danjuma Goje ta rasu

Allah Ya yi wa matar tsohon Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Yelwa Mohammed Danjuma Goje rasuwa a safiyar yau (Litinin) tana ‘yar shekara 55. An samu…

Allah Ya yi wa matar tsohon Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Yelwa Mohammed Danjuma Goje rasuwa a safiyar yau (Litinin) tana ‘yar shekara 55.

An samu labarin rasuwar ne daga wani sanarwa da dan tsohon gwamnan, Ahmed Mohammed Goje ya fitar, inda ya ce ta rasu ne a wani asibiti a kasar Amurka.

Hajiya Yelwa ta rasu ta bar Maigidanta, Sanata Danjuma Goje, ‘ya’ya shida, jikoki 10 da ‘yan uwa da abokanan arziki.