✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsohuwar Kwamishina a Kano Zubaida Damakka ta rasu

Har zuwa lokacin rasuwarta, ita ce Manajar Kamfanin Madara na L&Z.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Allah Ya yi wa Barista Zubaida Damakka Abubakar rasuwa a wannan Asabar din.

Ta rasu ne yau Asabar bayan ta yi wata ’yar takaitacciyar jinya a Abuja.

Za a yi jana’izar ta a gobe Lahadi da karfe 9 na safe a gidansu da ke Unguwar Gwammaja a birnin Kano.

Marigayiyar tsohuwar kwamishina ce a Ma’aikatar Harkokin Mata da Ma’aikatar Kasafi da Tsare-Tsare ta Jihar Kano.

Haka kuma, har zuwa lokacin rasuwarta, ita ce Manajar Kamfanin Madara na L&Z.

Aminiya ta ruwaito cewa, Barista Zubaida na daya daga cikin kwamishinoni biyar da tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sauke a watan Oktoban 2017.