✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya sa hannu kan dokar kara albashin alkalai da 300%

A ranar Talata shugaban kasar ya sa hannu kan dokar karin albashi alkalai da kashi 300%

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sa hannu kan dokar kara albashin alkalai da ninki uku.

Mashawarcin Shugaban Kasa kan Harokin Majalisa Basheer Lado, ya bayyana cewa a ranar Talata shugaban kasar ya sanya hannu kan dokar karin albashi alkalai da kashi 300%

A watan Jun ne Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da kudurin dokarin karin albashin alkalai da kashi 300%, wanda shugaban kasa ya aike mata.

Sanata Lado ya bayyana rattaba hannu kan kudirin da shugaban kasar ya yi a matsayin wani gagarumin nasara da kuma ke nuna jajircewarsa wajen kyautata rayuwar ma’aikatan Najeriya.

Lado ya kuma bukaci alkalai a kasar da su kara himma wajen ganin an tabbatar da adalci da kuma gaggawa.