✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya mika kudurin karin albashi zuwa N70,000 ga Majalisa

Shugaba Tinubu ya mika kudurin karin mafi karancin albashi zuwa N70,000 ga Majalisa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika kudurin karin mafi karancin albashi zuwa N70,000 ga Majalisar Dokoki ta Kasa.

A ranar Talata shugaban ya mika kudurin karin albashin domin amincewar majalisa dokokin kasa kafin ya zama doka a fara biyan albashin.

Shugaban kasar ya bukaci majalisar ta hanzarta amincewa da kudurin na karin albashi, domin zama doka da kuma aiwatarwa.

Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio da takwaransa na Majalisar Wakilai Abbas sun samu wasikar kudurin da ke neman amincewar mambobin majalisun.

N70,o00 shi ne mafi karancin albashin da shugaban kasar da kugniyoyin kwadago suka amince a kara daga Naira 30,000, bisa sharadin za a rika karawa bayan duk shekaru uku.

Shugaban kasan ya kuma aike wa majalisar da bukatar yin gyara ga dokar aikin dan sanda domin dacewa da Sashe na 58 na kudin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da aka yi wa gyaran fuska.

Gyaran da za a yi na da alaka da batun karfin ikon nadawa da kuma wa’adin shugaban ’yan sandan Najeriya.