✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ne da kansa zai bayyana sabuwar ranar da za a yi kidayar jama’a – NPC

Hukumar ta ce Tinubu ne zai sanar da ranakun nan ba da jimawa ba

Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ce Shugaban Kasa Bola Tinubu ne da kansa zai bayyana sabbin ranakun da za a gudanar da kidayar jama’a da gidaje a Najeriya.

Shugaban hukumar, Nasir Isah Kwarra ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, bayan ya jagoranci tawagar hukumar domin yin bayanin inda suka kwana ga Shugaba Tinubu a fadar Aso Rock da ke Abuja.

Ya ce ya zuwa yanzu, hukumar ta mika rahotonta ga Shugaban, kuma shi take jira ya yi nazari a kai sannan ya yanke hukunci kan lokacin da za a gudanar da ita.

Sai dai ya ce saboda tsawon lokacin da ake dauka, bukatun hukumar na karuwa, don haka akwai yuwuwar su bukaci karin kudi a nan gaba.

Ya ce, “Mun yi masa cikakken bayani a kan shirye-shiryenmu, kuma muna farin ciki Shugaban ya nuna a shirye yake ya tallafa wa dukka tsare-tsarenmu 100 bisa 100 kan dukka bukatunmu.

“Saboda haka, mu za mu je mu ci gaba da shirye-shiryenmu, kuma za a ji daga bakinsa, ranakun da za a yi kidayar a nan gaba, saboda mu mun riga mun mika masa rahoto, zai kuma yi nazari a kai.

“Amma dai ya ba mu tabbacin tallafa mana, kuma muna gode masa a kan haka, musamman la’akari da muhimmancin kidaya wajen tsare-tsaren ci gaban kasa,” in ji Nasiru Kwarra.