Jam’iyyar adawa ta PRP ta tsaida Malam Salihu Sagir Takai, a matsayin dan takarar Gwamnan jihar Kano a zaben 2019.
Shugaban jam’iyyar PRP na jihar Alhaji Sammani Shariff ne ya bayyana wa manema labarai cewa, jama’iyyar ta tsaida Sagir Takai a matsayin dan takarar Gwamnan jihar Kano bayan tattaunawar da shugabannin jam’iyyar suka yi ranar Talata.