Shugabannin babbar jam’iyyar adawa ta PDP zasu tattauna a yau a sakatariyar jam’iyyar ta kasa a Abuja.
Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar Kola Ologbondiyan ne ya bayyana hakan jiya a Abuja.
Rahotanni na bayyana cewa, tattaunawar da jam’iyyar zata yi nada alaka ne, da shirin zaben Gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi, da kuma batun shigar da karar dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Atiku Abubakar.