Jam’iyyar APC ta kaddamar da kwamiti karkashin jagorancin Gwamna Kashim Shettima na Jihar Barno wanda zai gudanar da zaben fiidda dan takarar gwamna a zaben da z a a yi a jihar Anambara.
Zaben fidda gwanin wanda ’yan takara 12 ke neman tsayawa za a gudanar da shi ne a ranar Asabar 26 ga watan Agusta.
A hannu daya kuma jam’iyyar ta kafa kwamitin sauraren korafe-korafe karkashin jagorancin Dokta Hassan Lawal.
Sakataren shirye-shirye na Kasa na Jam’iyyar APC, Sanata Osita Izunaso shi ne ya kaddamar da kwamitocin biyu a jiya a Sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja.
Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan kaddamar da kwamitocin, Gwamna Shettima ya ce shi da kansa tare da shugaban sauraren korafe-korafe babu dan takarar da zai iya jan ra’ayinsu.
Ya bayyana cewa kwamitin a shirye yake ya gudanar da zaben fidda gwani na gaskiya a jihar.
Da aka tambaye shi ko ta yiwu wani dan takara ya ja ra’ayinsa? Sai ya ce “Ku kalle ni, shin kun ga alamar farashi a jikina? Gaskiyar al’amari shi ne ina tare da dattijo wanda za mu yi aiki tare, Dokta Hassan Lawal shi ma babu alamar farashi a wuyansa shi ne shugaban kwamitin korafe-korafe. Za mu yi aiki tare a Anambara tare da tawagarsa”.