✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Saura ƙiris Matawalle ya karɓi kujerarsa a Zamfara — APC

A ranar Juma'a ne kotun daukaka kara ta ayyana zaben Zamfara a matsayin 'Inconclusive'.

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na yankin Arewa maso Yamma, Garba Muhammad Datti, ya ce nan ba da jimawa ba tsohon Gwamnan Zamfara kuma Karamin Ministan Tsaro, Bello Muhammad Matawalle zai karɓi kujerarsa.

Datti, ya ce hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a ranar Juma’a, wanda ya tsige gwamna Dauda Lawal na jam’iyyar PDP, ya ba da kwarin gwiwa tare da karfafa fatan samun nasara a Kotun Koli.

Aminiya ta ruwaito cewa kotun daukaka kara a ranar Juma’a ta soke nasarar da Gwamna Lawal ya samu a zaben watan Maris tare da ba da umarnin sake zabe a kananan hukumomi uku a jihar.

Malam Musa Mailafiya Mada, Sakataren yada labarai na jam’iyyar APC shiyyar Arewa maso Yamma, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce mataimakin shugaban yankin Arewa maso Yamma na kasa, Garba Muhammad Datti, ya kuma yaba wa Matawalle bisa nasarar da ya samu, yana mai bayyana hakan a matsayin muhimmin mataki na kwato hakkinsa.

Nasarar, a cewarsa, ta tabbatar da kalubalen da jam’iyya mai mulki ta yi na samun nasarar PDP a kotu.

Ya bayyana cewa matsayin kotun daukaka kara na cewa kotun sun kasa gabatar da sahihan shaidu game da kararsu.

Wannan hukunci dai ya janyo rudani a jihar tare da haifar da cece-kuce kuce.

Tuni wasu suka fara kiranye-kiranye tare da suka kam cewar jam’iyyar APC mai mulki na neman danne komai a Najeriya ciki har da dimokuradiyya.