Rahotanni na bayyana cewa, rikici ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyar APC da PDP a garin Agwatashi da ke karamar hukumar Obi a jihar Nasarawa.
Rahotan na bayyana cewa, rikicin ya barke ne lokacin da `yan APC suka ziyarci yankin da ake ganin magoya bayan jam’iyyar adawa ta PDP tafi karfi.
An dai ta harbeharben bindiga lokacin rikicin.