✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ribers United ta kai ziyara birnin Madrid don samun horo

Kulob din Ribers United ta tafi kasar Sifen inda ta kai ziyara birnin Madrid don samun horo a kokarin tunkakar kakar wasa ta bana. Kulob…

Kulob din Ribers United ta tafi kasar Sifen inda ta kai ziyara birnin Madrid don samun horo a kokarin tunkakar kakar wasa ta bana.

Kulob din ya bar kasar nan ne a ranar Talatar da ta wuce da misalin karfe 2 da minti 35 na rana daga filin sauka da tashin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Tun a ranar 1 ga watan Nuwamban wannan shekara da muke ciki ne kulob din ya fara yin atisaye don tunkarar kakar wasa mai zuwa. Kulob din ya samu nasarar lashe kofin Super 4 da aka yi a Enugu da hakan ta sa yake fatan zai haskaka a kakar wasa mai zuwa.
Wannan nasara da kulob din ya samu ce ta sa ya yanke shawarar tafiya Sifen don yin balaguro a birnin Madrid. Ana sa ran zai buga wasannin sada zumunta a can don karfafa wa ’yan kwallonsa gwiwa kafin ya dawo Najeriya.
Sannan idan suka dawo Najeriya za su zauna a Abuja na wadansu kwanaki kafin su zarce zuwa Kaduna don cigaba da samun horo kafin daga bisani su koma Fatakwal.
A ranar 15 ga watan Janairun 2017 ne ake sa ran za a fara gasar firimiyar Najeriya. A bara Enugu Rangers ce ta zama zakara a gasar a karon farko bayan shekara 32 rabonta da kofin.